Wapharun l best forum updates
Would you like to react to this message? Create an account in a few clicks or log in to continue.

BUHARI 12 A WATANNI 12 RAHOTON MUSAMMAN: Nasarorin Shugaba Buhari 12 A Watanni 12

Go down

BUHARI 12 A WATANNI 12 RAHOTON MUSAMMAN: Nasarorin Shugaba Buhari 12 A Watanni 12 Empty BUHARI 12 A WATANNI 12 RAHOTON MUSAMMAN: Nasarorin Shugaba Buhari 12 A Watanni 12

Post by Admin Mon Jun 06, 2016 6:31 am

:cyclops:Yayin da gwamnatin Shugaba
Muhammadu Buhari ke shirin cika
shekara daya, shin ko da hawansa
mulki abubuwa sun ci gaba da
kasancewa kamar yadda suke a baya?
babu shakka amsar ita ce, a’a. Daga ranar 29 ga watan Mayun 2015,
ranar da aka rantsar da Shugaba Buhari
zuwa yanzu, ko shakka babu abubuwa
sun canja kwarai da gaske. A lokacin da
yake yakin neman zabe daga watan
Janairun 2015 zuwa watan Maris, Shugaba Buhari ya yi wa ‘yan Nijeriya
alkawarin cewa, idan Allah (S.W.T) Ya ba
shi nasara, zai fi maida hankali a kan
abubuwa uku, su ne; tsaro, kawar da cin
hanci da rashawa da kuma bunkasa
tallalin arziki, kan hakan idan aka ce Shugaba Buhari ya samu nasara fiye da
kaso 80 cikin 100, ba a yi kuskure ba,
ganin yadda gwamnatinsa ta samu
gagarumar nasara a wadannan
bangarori. Idan mai karatu na biye da ni,
ina nan zane da nasarori 12 a watanni 12 kamar haka: 1. Tsaro; lallai tsaro shi ne lamba daya a cikin skowace al’umma a duniya, lokacin
da shugaba Buhari ya karbi ragamar
jagorancin Nijeriya, tsaron kasar na
kokarin kubucewa ne daga hannun
mahukunta, domin kuwa wani sashe na
Nijeriya da ya kai girman kasar Belgium baki daya na hannun ‘yan ta’addan
Boko Haram, a wancan lokaci dukkan
kananan hukumomi 14 na jihar Borno
da guda 3 daga jihar Adamawa, na
karkashin ikon Boko Haram, su ke da
iko da kananan hukumomin, hasali ma sun cire tutocin Nijeriya tare da maye
gurbi da tutocinsu. Kazalika suka canja
sunayen kananan hukumomin, cikin
watanni 12 hakan ya zama tarihi,
dukkan wadannan kananan hukumomi
sun dawo karkashin ikon Nijeriya, dubban mutanen da suka yi gudun
hijira daga jihohin a yanzu sun koma
muhallinsu, zaman lafiya ya dawo,
gidajen da ‘yan Boko Haram suka
rurrushe yanzu ana sake gigginawa,
kasuwannin garuruwan duka an bude su, rayuwa ta koma kamar yadda take a
baya. 2. Kubutar da mutane sama da 12,000 daga hannun Boko Haram, kafin zuwan
Shugaba Buhari, bayan kubucewar
tsaro a kusan gaba dayan yankin Arewa
Maso Gabas, dubban mutane, manya,
yara, maza da mata sun shiga hannun
‘yan Boko Haram a matsayin bayi, amma a ranar da ya karbi ragamar mulki,
Shugaba Buhari ya fara canja fasalin
tsaro, ya bada umarnin mayar da manya
madafun iko na rundunar sojojin kasar
nan zuwa Maiduguri, wannan ya
taimaka wajen tabbatar da dawowar tsaro a yankin, sakamakon haka
rundunar jami’an tsaron Nijeriya sun
kubutar da mutanen da Boko Haram
suka sace ta karfi da yaji fiye da dubu 12
a cikin watanni 12. Bayan kubutar da
dubban mutanen, gwamnatin Muhammadu Buhari a yanzu ta maida
hankali wajen ganin sun koma
rayuwarsu cikin walwala fiye da yadda
suke yi a baya. 3. Matatun man fetur; kafin zuwan Shugaba Buhari matatun man da muke
da su a kasar nan, da suka hada da;
Matatar Port Harcourt, jihar Ribers, Warri,
Jihar Delta da kuma ta jihar Kaduna,
dukkanin su ba wadda take ba da mai
koda kuwa lita daya, kuma sun kasance a hakan shekara da shekaru, daga
zuwan gwamnatin Buhari, matatun
duka sun dawo aiki cikin kankanin
lokaci duk da yawan masu yi musu
zagon kasa, a yanzu haka dukkan su na
aiki, suna kuma tace mai fiye da lita milyan 7 a rana, sai dai kash, makiyan
Nijeriya da ci gabanta sun kassara
aiyukan matatun ta hanyar farfasa
hanyoyin da suke kai danyen man daga
inda ake hakowa zuwa inda ake tacewa.
Koda yake tuni gwamnatin Shugaba Buhari ta ba da umarnin bin duk hanyar
da suka dace wajen gyarawa tare da
kare faruwar hakan a nan gaba. Cikin
watanni 12, gwamnatin Buhari ta yi
abun da gwamnatocin baya suka kasa
yi a shekaru fiye da 12. 4. Tallafawa jihohi da kudaden biyan ma’aikata albashi; a lokacin da Shugaba
Buhari ya karbi ragamar mulkin kasar
nan, fiye da rabin jihohin kasar ba sa iya
biyan ma’aikatansu albashi, hakan ya yi
matukar tayarwa Shugaba Buhari
hankali kasancewarsa shugaban talakawa, ya kuma san yadda hakan zai
haifar da kunci da rashin walwala a
zukatan ma’aikatan musamman kanana,
wannan ya sa a watan Satumbar da ya
gaba, ya bada umarnin fitar da naira
bilyan 689.5 da babban bankin kasa na CBN, don rabawa jihohi 27, a matsayin
tallafi don

Admin
Admin

Posts : 3
Join date : 2016-06-05

https://wapharun.board-directory.net

Back to top Go down

Back to top

- Similar topics

 
Permissions in this forum:
You cannot reply to topics in this forum